Sarkin Dutse Yusufu Atakalafiya 1609 – 1616
Gabatarwa
Sarki Yusufu shi ne sarkin Dutse na goma sha biyar. Shi ne shugaban rundunar mayaƙan Dutse (sarkin yaƙi) a zamanin Sarki Jarmai Babba. Sarki Yusufu bashi da wata dangantaka ta jini da sarakunan da suka gaba ce. Kafin zamowarsa sarki a garin Takalafiya yake zaune. Mahaifansa kuma mutanen Zai ne.
Wannan suna na Takalafiya kuwa ya samo asali ne saboda samuwar kunamu da macizai a ƙarƙashin duwatsun da ke kan hanyar zuwa gidansa.
Sarki Yusufu shugaba ne na jama’a, mutum ne mai son sulhu. Garuruwa da dama sun mara masa baya a yunƙurinsa na haɓɓaka tattalin arziƙin Masarautar Dutse. Sarki Yusufu mutum ne mai tsantseni game da dukiyar jama’a.
Wasu mutanen da ba a san ko su waye ba, su suka kashe shi ta hanyar kisan gilla a shekarar 1616. Bayan rasuwarsa iyalansa sun ci gaba da rayuwa a wancan gida nasa da ke Takalafiya. Haka nan kuma gidan ya ci gaba da wanzuwa har lokacin da sarki Sulaimanu II (1923 – 1960) ya mayar da gurin maƙabarta bisa umarnin Turawa dan hana jama’a binne/bisne gawarwaki a gidajensu saboda dalilan kiwon lafiya.
Manazarta:
NNPC (2007). Hausawa da Maƙwabtansu, Littafi na Biyu. Northern Nigerian Publishing Company Limited, Zariya, Najeriya.
Sanusi N.M. (2015). Stories of Dutse Palace, 1421 - 2009. An buga a Maɗaba'ar Jahar Jigawa, Najeriya.
Sanusi N.M. (2015). The Days in My Life. An buga a Maɗaba'ar Jahar Jigawa, Najeriya.
Sarakunan Dutse
Haɓawa
- Tuwai
- Ƙetare
- Tasau
- Maido
- Maigiji-Tandu
- A Maranje
- Babilu
- Labun
- Yakwabu
- Sambore
- Dunhu
- Akuli
- Mantau
- Jawandu-Dogo
- Yusufu
- Mamman
- Yakubu
- Inuwa
- Habu
- Audu
- Mani6
- Hassan
- Mamman
- Yahai
- Ada
- Zubairu
- Mamman
- Amadu
Fulani
- Salihu
- Musa Ahmadu
- Bello
- Suleman
- Ibrahim
- Abdulƙadir
- Salihu
- Ibrahim
- Abdulƙadir
- Abduƙadir
- Haladu
- Halilu
- Hamidan
- Abdullahi
- Bello
- Suleman
- Abdullahi
- Muhammadu
- Nuhu M.S.
Tura wannan shafi zuwa ga abokai ta:
TweetLatsa madannin "Like" ka nuna goyon baya ko kuma "Share" ka yaɗa shafin